1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

'Yan ci ranin Sudan 13 sun mutu bayan kifewar kwale-kwalensu

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
February 9, 2024

Kasashen Tunisiya da Libiya sun kasance babbar hanyar da masu tsallakawa Turai ta barauniyar hanya ke bi, inda bara kadai hukumomin Tunisiyan suka samu nasarar cafke 'yan ci-rani kusan dubu saba'in da ke kokarin ketarawa

https://p.dw.com/p/4cECa
Hoto: MINDS Global Spotlight/AP/Santi Palacios/picture alliance

'Yan ci ranin Sudan 13 ne suka mutu bayan da kwale-kwalen da suke ciki ya kife a gabar ruwan Tunisiya yayin da wasu 27 suka yi batan dabo, a kokarinsu na tsallakawa zuwa Turai ta barauniyar hanya, kamar yadda kamafanin dillancin labaran Faransa AFP ya ruwaito.

Karin bayani:Muhawara kan takaita bakin haure a Faransa

Mai magana da yawun kotun birnin Monastir Farid Ben Jha ya shaida wa kotun cewa daga cikin fasinjoji 42 da suke jirgin, biyu kacal aka tarar a raye, kuma ana ci gaba da neman sauran da suka lume a ruwa, bayan sun taso daga garin Jebiniana kusa da birnin Sfax, sakamakon kazantar yakin basasa a Sudan.

Karin bayani:An gano gawarwakin 'yan ci-rani guda biyu a cikin jirgin ruwan da ke dauke da mutane sama da 200 a Spain

Kasashen Tunisiya da Libiya sun kasance babbar hanyar da masu tsallakawa Turai ta barauniyar hanya ke bi, inda bara kadai hukumomin Tunisiyan suka samu nasarar cafke 'yan ci-rani kusan dubu saba'in da ke kokarin ketarawa.