1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: An fara koyar da harshen Rashanci a cikin makaratu

Gazali Abdou Tasawa AH
April 9, 2024

A wani mataki na karfafa sabuwar huldar dangantakar da ta hada kasar ta Nijar da Rasha tun bayan da sojoji suka karbi mulki kasar Rashar ta bude sashen koyar da harshen Rashanci a jami'ar Yamai.

https://p.dw.com/p/4eaC9
Hoto: Gazali/DW

 Dalibai kimanin 25 ne maza da mata ke zama rukunin farko na daliban jami'ar ta birnin Yamai da suka yi rijista ke  koyon harshen Rashanci a sabuwar cibiyar koyon wannan harshen da ke zama irinta ta farko a kasar. Kuma wasu daga cikin daliban sun bayyana farin cikinsu da tsarin da kuma burin da suke son cimma a cikin koyon  harshen 

Tawaga ta musammun ta zo dagá Rasha domin girka sashen koyon Rashanci a cikin makarantu

Niger Niamey 2024 | Beginn des Russischunterrichts an Schulen
Hoto: Gazali/DW

Tawaga ce dai ta musamman daga jami'ar patrice  Lumumba ta birnin Moscou ta iso a kasar ta Nijar domin kaddamar da wannan cibiya ta koyar da harshen Rashanci a jami'ar Abdoulmoumouni ta birnin Yamai. Parfesa Khabiba Shagbanova ta jami'ar Moscou kana shugabar sashen kula da huldar harkokin ilimi tsakanin Rasha da Afirka ita ce jagoran tawagar. '' Bude cibiyar koyar da harshen Rashanci na taimaka wa ga karfafa huldar kasashenmu biyu a fannin raya al'adu da ilimi. Sati biyu kenan da muka zo nan , mun yi nasara samun dalibai masu yawa da ke da sha'awar koyon Rashancin. Yanuzu haka akwai kamar dalibai 25 maza da mata da ma malamansu wadanda suka yi rijista a sashen koyon   Rashanci.